Azumi[1] shi ne kamewa[2] daga barin cin abinci ko sha ko jima'i (saduwan tsakanin namiji da mace) ko shan taba ko allura ta abinci daga ketowar alfijir nabiyu har zuwa faduwan rana. Hakika Allah ya wajabta azumi acikin Alkur'ani mai girma inda yace "duk wanda ya riski watan (Ramadan) to ya azumceshi" shi Musulmi ne (surah albakarah 2:185) sannan ya kara da cewa "ya ku masu imani hakika an wajabta muku azumi kamar yanda akawajabta ma wanda suke gabaninku koku zakuyi takawa" (albakarah 2:183)

Azumi
human behavior (en) Fassara da dietary restriction (en) Fassara
Bayanai
Ƙaramin ɓangare na abstinence (en) Fassara
Amfani religious rite (en) Fassara, trance (en) Fassara, weight loss (en) Fassara da Azumi
WordLift URL (en) Fassara http://data.medicalrecords.com/medicalrecords/healthwise/fasting

Abubuwanda suke karya azumi gyara sashe

  1. Cin abinci
  2. Shan abinsha
  3. Jima'i
  4. Shantaba
  5. Alluran abinci da dai sauran dukkan abinda zai bi ta makoshin mai azumi

Azumi akwai wanda yake wajibi (farillah)akwai kuma na Nafila wato sunnah, Azumin wajibi wato na Farilla shine Azumin watan Ramadan, Azumin kaffara da kuma Azumin balance. Shi na Ramadan indai ya riski Musulmi yanada lafiya, da hankali, kuma baligi (Balaga) wanda ya ke mazaunin gida ma'ana ba matafiyi ba, kuma ba lokacin jinin al'ada ba ga mata ko kuma Jego ko kuma tsohon da tsufa yasa baya iya yin Azumi, ko kuma wani dalili mai ƙarfi wanda ma'abota Ilimin addinin Musulunci sukayi fatawa a kanshi. Sai Azumin Nafila kamar azumin Litinin da Alhamis sai kuma sauran azumin Nafila waɗanda suma sanannu ne. Sai azumin bakance shi ma wajibi ne, amma don sanin haka sai a tambaya Malaman Musulunci Masu riƙon sunnah waɗanda keyi don Allah. Ina ƙara nanata wa azumin watan Ramadan wajibi ne[3] don saboda haka Ayoyin Alqur'ani mai girma da sukayi nuni da hakan. Anason a lokacin Azumin watan Ramadan mutum ya yawaita Ibadu kamar yawan karatun Alqur'ani, sadaƙa, zumunta, Istigfari, yawan nafila musamman Sallah tarawihi Tahajjud da kuma kiyaye jam'i Sallolin Farilla da dai sauran Ibadu da shari'a ta bada umarnin yin su. Don Karin bayani akan Azumi a duba littafin (Iziyya da Risala).

Abubuwan Dake Sawa A Ajiye Azumi gyara sashe

1. Ya wajaba ga mai al’ada da mai jinin haihuwa su ajiye azumi.[4]

2. Wanda ke so ya tsamo wani daga halaka da suransu.[5]

3. Matafiyi an halasta masa yin kasru kuma an sunnan ta masa ajiye azumi.[6]

4. Maralafiya wanda ke tsoron cutuwa.

5. Mazaunin gida wanda ya yi tafiya da rana, abunda ya fi shi ne ya yi azumi don fita daga cikin sabani.

6. Mai-ciki da mai shayarwa, wadanda suka ji tsoron cutarwa a karankansu ko a dan su, koda sun ajiye azumi don tsoran ‘ya’yan su, waliyan su za su ciyar da miskini a kowanne yini bayan haka za su ranka azumi.

Manazarta gyara sashe