Asusun Tallafawa Noma na Duniya

Asusun Ci Gaban Aikin Noma na Duniya ( IFAD ; French: Fonds international de développement agricole (FIDA)) cibiyar hada-hadar kudi ce ta kasa da kasa ta kasance kuma hukuma ta musamman ta Majalisar Dinkin Duniya da ke aiki don magance fatara da yunwa a yankunan karkara na kasashe masu tasowa. Ita ce kungiya daya tilo da ta ke maida hankali kan tattalin arzikin karkara da samar da abinci.[1]

Asusun Tallafawa Noma na Duniya

Bayanai
Iri specialized agency of the United Nations (en) Fassara
Masana'anta international governmental or non-governmental organizations (en) Fassara
Ƙasa Italiya
Mulki
Hedkwata Roma
Tarihi
Ƙirƙira 1977

ifad.org


International Fund for Agricultural Development

Bayanai
Gajeren suna IFAD
Iri United Nations specialised agency
Masana'anta international governmental or non-governmental organizations (en) Fassara
Ƙasa Italiya
Mulki
Hedkwata Rome, Italy
IFAD.png
Tarihi
Ƙirƙira 1977

ifad.org


Ambassador McCain sees joint food, nutrition, and resilience work in Laos
Tambari
500 Lire IFAD

Hedikwatarta na a Birnin Rome, IFAD na da ayyukan tallafi a sama da 200 a kusan ƙasashe 100.[2] Tana ba da kuɗi da daukar nauyin tsare-tsare masu inganta tsarin kula da ƙasa da ruwa, haɓaka ababen more rayuwa na karkara, horarwa da ilimantar da manoma kan ingantattun fasahohi, haɓaka juriya kan sauyin yanayi, haɓaka samun kasuwa, da makamantansu.[3]

IFAD tana da membobin kasashe guda 177 kuma tana aiki tare da kungiyar kasashe masu arzikin man fetur (OPEC) da mambobin kungiyar hadin kan tattalin arziki da ci gaba (OECD). Tun da aka kafa ta a 1977, IFAD ta ba da dala biliyan 22.4 na lamuni da tallafi kuma ta haɗu da ƙarin dalar Amurka biliyan 31 a cikin haɗin gwiwa na ƙasa da ƙasa.

Tarihi gyara sashe

An kafa IFAD a matsayin cibiyar hada-hadar kudi ta duniya a cikin shekarar 1977 ta hanyar kuduri na Majalisar Dinkin Duniya mai lamba 32/107 (30 Disamba 1977) a matsayin daya daga cikin manyan sakamakon taron samar da abinci na duniya na 1974. [4] Hedkwatarta tana nan a birnin Rome na kasar Italiya, kuma memba ce ta kungiyar raya kasashe ta Majalisar Dinkin Duniya.[5] Shugaban IFAD na yanzu shine Alvaro Lario daga kasar Spain, wanda ya karbi mulki daga hannun Gilbert Houngbo a karshen shekara ta 2022.[6]

Duba kuma gyara sashe

 

  • Tsaron abinci
  • Cibiyoyin Kuɗi na Ci gaba
  • TSORO

Manazarta gyara sashe

  1. "IFAD at a glance". IFAD. Retrieved 28 August2020.
  2. "IFAD at a Glance"
  3. "Topics". IFAD. Retrieved 28 August 2020.
  4. Empty citation (help)
  5. "UNDG Members". United Nations Development Group. Archived from the original on 11 May 2011. Retrieved 15 May 2012.
  6. "Alvaro Lario, global finance executive, takes helm at UN's International Fund for Agricultural Development". IFAD. 30 September 2022. Retrieved 17 December 2022.

Hanyoyin haɗi na waje gyara sashe

Template:United NationsTemplate:ECOSOC