Kayode Egbetokun
Rayuwa
Haihuwa 1964 (59/60 shekaru)
Sana'a

Kayode Egbetokun (an haife shi a watan Satumba shekarar ta alif ɗari tara da sittin da hudu (1964), ɗan sandan Najeriya ne wanda shi ne Sufeto Janar na ‘yan sanda na yanzu kuma na 22. Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ne ya nada shi ne a matsayin cike gurbin Usman Alkali Baba .

Rayuwar farko da ilimi gyara sashe

An haifi Egbetokun ranar 4 ga watan Satumba na shekarar 1964 a Erinja, karamar hukumar Yewa ta Kudu a jihar Ogun. Ya kammala karatunsa na farko a Jami'ar Legas, Akoka, da digiri na farko a fannin lissafi a watan Yuni shekarar 1987 sannan ya karantar da lantarki ilimin lissafi a takaice a Kwalejin Fasaha ta Yaba . Ya yi digiri na biyu a fannin Injiniya Analysis daga Jami’ar Legas a shekarar 1996, sannan ya yi digiri na biyu a fannin tattalin arzikin man fetur daga Jami’ar Jihar Delta a shekarar 2000, da MBA daga Jami’ar Jihar Legas, Ojo a shekarar 2004. Ya kuma yi digirin digirgir a fannin zaman lafiya da tsaro a Jami’ar Al-hikmah, Ilorin, Jihar Kwara.

Sana'a gyara sashe

Egbetokun ya shiga aikin ‘yan sandan Najeriya a ranar 3 ga watan Maris na shekarar 1990 a wager matsayin Mataimakin Sufurtandan ‘yan sanda na Cadet. A matsayinsa na mataimakin Sufeton ‘yan sanda a shekarar 1999, an nada shi babban jami’in tsaro ga zababben kwanturaginsa gwamnan jihar Legas, Bola Tinubu, wanda yanzu ya zama shugaban Najeriya.

Ya yi aiki a matsayin Kwamanda, Rapid Response ringing Squad (RRS), Lagos, egurinsi Squadron Commander, MOPOL, Anti-Fraud Unit, FCT Command, Abuja, Babban Sufeton 'yan sanda, Gudanarwa, Hedkwatar Rundunar Jihar Legas, Ikeja, Kwamandan Area, Osogbo. Old fashioned with Kwamandan Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Osun, Gusau, Jihar Zamfara.

A ranar 19 ga watan Yunin shekarar 2023, shugaba Tinubu ya nada Egbetokun ya maye gurbin Usman Alkali Baba. Har zuwa lokacin da aka nada shi a matsayin Sufeto-Janar, ya kasance mataimakin sufeto-Janar na ‘yan sanda kuma mai kula da DIG na shiyyar Kudu-maso-Yamma, don jagorantar sashin binciken manyan laifuka (FCID), hedkwatar rundunar, Abuja tun ranar 6 ga watan Afrilu shekarar 2023. [1]

Manazarta gyara sashe

  1. Cite error: Invalid <ref> tag; no text was provided for refs named Van