Hukumar Jarabawa ta Kasa (Nijeriya)

Hukumar gudanar da Jarabawar NECO

Hukumar Jarrabawa ta kasa (wadda aka fi sani da NECO) ƙungiya ce ta jarabawa a Najeriya wacce ke gudanar da jarrabawar Sakandare da kuma babban satifiket na shaidar ilimi a watan Yuni/Yuli da Nuwamba/Disamba.

Hukumar Jarabawa ta Kasa
Bayanai
Gajeren suna NECO
Iri ma'aikata
Used by
Tarihi
Ƙirƙira ga Afirilu, 1999
neconigeria.org

Tarihi gyara sashe

Tsohon shugaban ƙasa Abdulsalami Abubakar ne ya ƙirƙiro NECO a watan Afrilu shekara ta 1999.[1] Ita ce ƙungiya ta farko ta Tarayya da ta ba da tallafin rajista ga masu neman ilimi a Najeriya.

Wajibi gyara sashe

Hukumar ta NECO dole ta ɗau nauyin ɗaukar ɗawainiyar hukumar auna ilimi ta kasa (NBEM). Jarabawar farko anyi ta ne a tsakiyar shekara ta 2000.[1]

Gudanarwa gyara sashe

Lokacin da Abubakar M. Gana ya ke jagorantar ƙungiyar, wanda shugaban ƙasa ya naɗa shi a ƙarƙashin doka mai sashe na 9 (1) na dokar kafa ƙungiyar.[2] Tana da sassa shida, kowane sashe na da darekta mai jagorancin sashen. Haka-zalika kowane Sashe yana da sassa, wanda ya ƙunshi rukuni. Tawagar daraktoci da masu rejista sune hukumar da ke ƙarƙashin jagorancin shugaba Abubakar Mohammed.[3]

Senior Secondary Certificate Examination (internal and external) gyara sashe

Najeriya na ba da ilimi na farko na shekaru shida, karatun karamar sakandare na shekaru uku, karatun sakandare na shekaru uku da karatun gaba da sakandare na shekaru hudu. Darussan Lissafi da harshen Ingilishi wajibi ne kodayake ƙila ba za a buƙaci ilimin lissafi ba don wasu darussa a manyan makarantu.

Basic Education Certificate Examination (BECE) gyara sashe

Basic Education Certificate Examination (BECE) ita ce babbar jarrabawar da za a yi don samun cancantar shiga makarantun sakandare da na sana'a a ƙasashen Ghana da Najeriya. Ana rubuta jarabawar bayan shekaru uku na sashen ƙaramar makarantar sakandarnko shekaru ukkun farko na makaranta sakandare-(Junior section 1, 2, 3).

Jarrabawar Shiga Kasa baki daya gyara sashe

Jarabawar Shiga gama-gari ta ƙasa ana yi wa ɗaliban da suka cika shekara ta 6 a matakin farko na ilimi don shiga Kwalejin Unity na Tarayya. Ana gudanar da jarrabawa biyu a shekara.[4]

A ranar 15 ga watan watan Yulin 2013 ne aka yi ta rade-radin cewa akwai shirye-shiryen da gwamnatin tarayyar Najeriya ta yi na cire Hukumar Jarabawa ta Kasa (NECO) daga tsarin ilimin Najeriya saboda karancin da matsakaitan kaso daga ƴan takara a fadin jihohi a Najeriya. Gwamnati ta yi gaggawar karyata waɗannan iƙirari ta hannun ministan ilimi na lokacin Mista Nyesom Wike.[5]

Tsarin Jarrabawar

Tambayoyin Jarabawar Jama'a ta Ƙasa sun ƙunshi kamar haka:

  • JARABAWA I
    • Sashe na A - Lissafi da Kimiyya na Gabaɗaya-(General Science)
    • Sashe na B - Turanci da Nazarin zamantakewa
  • JARABAWA II
    • Sashe na A – Quantitative da Vocational Aptitude
    • Sashe na B – Verbal Aptitude

Manazarta gyara sashe

  1. 1.0 1.1 "National Examinations Council (NECO): Introduction". Neconigeria.org. 2003-10-30. Retrieved 2014-05-14.
  2. NECO official website
  3. "FG Constitutes Boards of FMBN, FCDA, NECO, SON, Others, Articles". Thisday Live. 2013-01-01. Archived from the original on 2014-04-07. Retrieved 2014-05-14.
  4. "NECO Administrative Structure". Neconigeria.org. 2003-10-30. Retrieved 2014-05-14.
  5. "No plan to scrap NECO, UTME, Minister tells Senate". Vanguard News (in Turanci). 2013-04-18. Retrieved 2021-05-27.

Hanyoyin haɗi na waje gyara sashe