An haifi Emmanuel Agbadu Akabe a ranar 29 ga watan Nuwamba 1960 a karamar hukumar Doma ta jihar Nasarawa. Yanzu Haka Shine mataimakin Gwamnan Jihar Nasarawa.

KARATU gyara sashe

Emmanuel Akabe Ya yi makarantar firamare ta St.Mikel, Akwanga, jihar Nasarawa.
Bayan kammala karatunsa, ya wuce Kwalejin St.Joseph, Vom, Jihar Filato.  Ya kammala karatunsa na Likitanci a Jami'ar Jos a shekarar 1984.

Ya kammala aikinsa na gida a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos, (JUTH) a shekarar 1985, sannan ya yi hidimar bautar kasa (NYSC) a Asibitin Soja, Division 82 a Jihar Enugu, a 1986, bi da bi.[1]

An shigar da shi cikin Shirin Horon zama mai ba da shawara a 1986 a Asibitin Koyarwa na Jami'ar Jos, (JUTH).  Ya kammala horon ne a shekarar 1992 inda ya samu gurbin shiga ‘Fellowship of the National Postgraduate Medical Medical of Nigeria’.
Ya sami horo mai zurfi kan aikin tiyata da ciwon ido a Indiya. Ya yi karatu a Jami'ar Jos, Faculty of Medicine & Surgery, a cikin Janairu 1993-1995 kuma daga 1997-1999 ya koma sashen ilimin ido a matsayin mai hazaka da yawa[2]
Ya samu nasarar aikin nasa inda ya horas da kwararrun likitocin ido daga Asibitin Koyarwa na Jami’ar Jos (JUTH) zuwa Asibitin Kasa da ke Abuja.

Emmanuel Akabe ya yi nasarar hada sassa daban-daban na sashen kula da lafiya. A ranar 23 ga watan Agusta, 2013, Akabe ya taimaka wajen amincewa da gina manyan asibitoci guda uku da darajarsu ta kai biliyan 2.5 a jihar Nasarawa. Ya ce an yanke shawarar kafa karin manyan asibitoci a jihar domin rage cunkoso a asibitin kwararru na Dalhatu Araf (DASH) da ke Lafia, jihar Nasarawa.

Ya kasance kwararre ne a fannoni daban-daban, tun daga Association of Resident Doctors (ARD), JUTH da National Association of Resident Doctors (NARD) kuma daga karshe ya daukaka zuwa matsayin mataimakin shugaban Kungiyar na kasa na biyu.
A kungiyar likitocin Najeriya (NMA), ya rike mukamai da dama a reshen jihar Filato inda har ya kai ga zabensa a matsayin Sakatare kuma shugaban har wa'adi biyu da mataimakin babban sakataren kasa na tsawon shekaru biyar.
Ya kuma kasance ma'ajin kasa a karkashin jagorancin Dr. Kitchener.
A ranar 17 ga Afrilu, 2012, kungiyar likitocin Najeriya (NMA) a jihar Nasarawa ta karrama shi a matsayin kwamishinan lafiya na lokacin saboda gudunmawar da ya bayar wajen ayyukan raya kasa ga bangaren lafiya a jihar.
A shekarar 2013 kuma ya samu lambar yabo ta jami'ar Jos.
Dokta Emmanuel Akabe kwararren likitan ido ne wanda ke da kwarewa ta musamman wajen kula da cutar Glaucoma,

Dan siyasa ne na asali kuma tsohon mai kula da asibitin Filato wanda ya yi aiki a gwamnatin Gwamna Umar Tanko Al-makura a matsayin kwamishinan lafiya kuma babban jijiya wajen tabbatar da cewa an samu ci gaba a asibiti. lafiyar ‘yan kasa a lokacin barkewar cutar Ebola da zazzabin Lassa, kuma ya kasance mai bayar da shawarwari ga gina sabbin asibitoci, da farfado da tsarin kiwon lafiyar jihar Nasarawa da kuma rufe cibiyoyin lafiya sama da 126 da ke gudanar da ayyukan ba bisa ka’ida ba, a fadin jihar. Ya kuma tabbatar da cewa an karfafa tsarin kiwon lafiya na gwamnati da na masu zaman kansu da cibiyoyin kiwon lafiya na zamani.

An rantsar da Dr. Emmanuel Akabe a matsayin mataimakin gwamnan jihar Nasarawa 29 ga Mayu, 2019 .

Manazarta gyara sashe

  1. https://nasarawastate.gov.ng/deputy-governors-profile/
  2. https://sunnewsonline.com/dr-akabe-is-a-loyal-honest-professional-we-will-swim-together-to-succeed-gov-sule/