Bezabeh Meleyo Mekengo ( {{Lang-am </link> ; an haife shi a ranar 26 ga watan Yuni shekara ta 1995) ƙwararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne na ƙasar Habasha wanda ke taka leda a matsayin ɗan wasan tsakiya mai kai hari ga ƙungiyar Firimiya ta Habasha Fasil Kenema da kuma ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Habasha .

Bezabeh Meleyo
Rayuwa
Haihuwa Habasha, 1995 (28/29 shekaru)
Sana'a
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
Ƙungiyoyi Shekaru Wasanni da ya/ta buga Ƙwallaye
 

Aikin kulob gyara sashe

Wolaitta Dicha gyara sashe

Meleyo ya fara aikinsa na ƙwararru da Wolaitta Dicha kuma ya fara buga wasa a kakar shekarar 2015–16 Premier League ta Habasha . A cikin shekarar 2017, ya lashe gasar cin kofin Habasha tare da kulob din.

Fasil Kenema gyara sashe

A ranar 1 ga watan Yuli shekarar 2019, Meleyo ya rattaba hannu da Fasil Kenema . Ya ci gasar Premier ta Habasha ta shekarar 2020-21 tare da kulob din.

Ayyukan kasa da kasa gyara sashe

Meleyo ya fara buga wasansa na farko a duniya tare da tawagar kasar Habasha a wasan sada zumunci da suka yi da Saliyo a ranar 26 ga watan Agusta shekarar 2021.

Girmamawa gyara sashe

Wolaitta Dicha

  • Gasar Cin Kofin Habasha : 2017

Fasil Kenema

  • Premier League : 2020-21

Manazarta gyara sashe

Hanyoyin haɗi na waje gyara sashe

Template:Ethiopia squad 2021 Africa Cup of Nations