Zainab Ummaru Musa Yar'adau itace uwar gidan Usman Sa'idu Dakin Gari tsohon Gwamnan Jihar Kebbi, asalin sunan ta shine Zainab Ummaru Musa Yar’adua. Ita yace ga marigayi tsohon Shugaban Kasa Alhaji Umaru Musa Yar'Adua. An haife ta 1 ga watan Oktoba, shekara ta 1979, a Jihar Katsina.[1]

Karatu gyara sashe

Tayi primary a Katsina Steel Rolling Staff School daga shekarar (1989) zuwa shekarar (1992). Tayi sakandire a Federal Government Girls Day College Bakori daga shekarar (1993 )zuwa shekarar (1996). Tayi kuma Essence International School, Kaduna daga shekarar (1996) zuwa shekarar (1999). Tayi Jami’ar Maiduguri daga shekarar( 2000 )zuwa shekarar (2002 )inda daga bisani tayi Huron University, London daga shekarar( 2003) zuwa shekarar (2006). Ta kuma yi Project Management College United Kingdom.[1]

Rayuwa gyara sashe

Ta buɗe ƙungiya taimakon mata da yara wacce ake kira ‘(ZADAF FOUNDATION FOR WOMEN AND CHILDREN)’.[1]

Bibiliyo gyara sashe

  • Furniss, Graham. (1996). Poetry, prose and popular culture in Hausa. International African Institute. Edinburgh: Edinburgh University Press for the International African Institute. ISBN 978-1-4744-6829-9. OCLC 648578425.

Manazarta gyara sashe

  1. 1.0 1.1 1.2 Furniss, Graham. (1996). Poetry, prose and popular culture in Hausa. International African Institute. Edinburgh: Edinburgh University Press for the International African Institute. p.p 173 ISBN 978-1-4744-6829-9.