Muḥammad Usmān Mansoorpuri (12 ga watan Agustan shekara ta 1944 zuwa 21 ga watan Mayu shekara ta alif dubu biyu da a shirin da daya 2021) masanin addinin ne a kasar Indiya wanda ya yi aiki a matsayin shugaban kasa na farko na Jamiat Ulama-e-Hind Mahmood. Ya koyar da hadith a Darul Uloom Deoband kuma ya yi aiki a makarantar a matsayin ma aikaci

Tarihin rayuwa shi

gyara sashe

An haifi Usmān Mansoorpuri a ranar 12 ga watan Agusta a shekara ta 1944 a Mansurpur, Muzaffarnagar . Ya kammala karatu daga Darul Uloom Deoband a cikin dars-e-nizami na gargajiya a shekarar 1965. Ya ƙware a cikin wallafe-wallafen Qirat, Tajweed da Larabci a shekara ta 1966 daga makarantar sakandare ta Deoband

Usmān ya koyar a Madrasa Qāsmia a Gaya, Bihar na tsawon shekaru biyar, a duniya kuma a Madarsa Islamiya Arabia, Amroha na tsawon shekaru goma sha ɗaya. A shekara ta 1982, an nada shi malami a Darul Uloom Deoband . Ya koyar da hadīth ciki har da littattafan Muwatta Imam Malik da Mishkat al-Masabih . A ranar 5 ga watan Afrilu shekara ta alif dubu biyu da takwas 2008, an nada shi Shugaban kasa na Jamat Ulama-e-Hind's Mahmood faction. Ya yi aiki a matsayin mataimakin shugaban Darul Uloom Deoband na tsawon shekaru goma sha ɗaya daga shekarar 1997 zuwa ta alif dubu biyu da takwas 2008. A watan Oktoba a shekara ta alif dubu biyu da shirin 2020, an nada shi shugaban aiki na seminary.Littattafansa sun haɗa da Radd-i Qādyāniyat . [1]

 
Mansoorpuri (tsakiya) tare da Firayim Minista na kasar Indiya Narendra Modi da Mahmood Madani .
  1. "Books by Muḥammad Usmān Mansoorpuri". WorldCat. Archived from the original on 22 May 2021. Retrieved 22 May 2021.