Tambayoyi Guda Hudu Da Za Ai wa Kowa Ranan Alqiyama
TAMBAYOYI GUDA HUDU DA ZA A YIWA KOWA A RANAR ALKIYAMA
![](http://upload.wikimedia.org/wikipedia/commons/thumb/e/e0/Icono_aviso_borrar.png/80px-Icono_aviso_borrar.png)
Annabi صلى الله عليه وسلم ya ce: "Ranar alkiyama digadigan bawa ba za su gushe ba har sai an yi masa tambayoyi guda hudu:
◾ Rayuwarsa: A me ya karar da ita
◾ Iliminsa: Me ya aikata da shi
◾ Dukiyarsa: A ina ya same ta, kuma yaya ya kashe ta
◾ Gangar jikinsa: Yaya ya yi amfani da ita."
Tirmidhi:2417, Darimi:537
Kowa sai ya yi shirin amsa wadannan tambayoyi.