Fatima Yelwa Danjuma Goje (An haife ta a shekara ta alif 1967) a kauyen Kashere na Jihar Gombe. Uwar gida ce ga tsohon Gwamnan Jihar Gombe.[1]

Fatima Yelwa Danjuma Goje
Rayuwa
Sana'a

Karatu gyara sashe

Tayi karatun primary dinta a kauyen Kashere (Kashere Primary School) a shekarun 80’s. Tayi certificate a Grade II Women Teachers College Azare.[1]

Rayuwa gyara sashe

Fatima ta auri mijinta Alhaji Danjuma Goje tun kafin ta gama karatun ta, a shekara 1981. A shekarar 2003, mijinta Danjuma Goje ya zama Gwamnan Jihar Gombe. Ta bude kungiya inda take tallafawa marasa galihu, yara mata da matasa wacce ake kira ‘THE WIDE FOUNDATION’ inda take hadun gwiwa da gwamnati da ma kungiyoyi masu zaman kansu don taimakon al’umma.[1]

Bibiliyo gyara sashe

  • Kabir, Hajara Muhammad,. Northern women development. [Nigeria]. ISBN 978-978-906-469-4. OCLC 890820657.
  • Furniss, Graham. (1996). Poetry, prose and popular culture in Hausa. International African Institute. Edinburgh: Edinburgh University Press for the International African Institute. ISBN 978-1-4744-6829-9. OCLC 648578425.

Manazarta gyara sashe

  1. 1.0 1.1 1.2 Furniss, Graham. (1996). Poetry, prose and popular culture in Hausa.International African Institute. Edinburgh: Edinburgh University Press for the International African Institute. p.p 182-183 ISBN 978-1-4744-6829-9.