Dandume

Karamar hukuma kuma gari a jahar Katsina, Najeriya.

Dandume (ko Dan Dume ) karamar hukuma ce a cikin jihar Katsina, Najeriya. Hedikwatarta kuma tana cikin garin Dandume da ke yammacin yankin. a11°27′30″N 7°07′37″E / 11.45833°N 7.12694°E / 11.45833; 7.12694.

Dandume

Wuri
Map
 11°25′00″N 7°12′00″E / 11.4167°N 7.2°E / 11.4167; 7.2
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
Jihohin NajeriyaJahar Katsina
Yawan mutane
Faɗi 145,323 (2006)
• Yawan mutane 344.37 mazaunan/km²
Labarin ƙasa
Yawan fili 422 km²
Bayanan Tuntuɓa
Kasancewa a yanki na lokaci

Tana da yanki na kimanin murabba'in km 422, da yawan jama'a 145,739 a ƙidayar shekara ta 2006. Sannan kuma mutanen karamar hukumar dandume suna gudanar da ayyukan noma, kiwo da kasuwanci. Mutanen karamar Dandume mutane ne masu al’adu iri ɗaya. Kuma Allah ya albarkacesu da masu ilimi boko da na zamani. Kama daga mahaddata Al Qur'ani Mai girma, karatun littattafai na Hadithi, Fikihu, larabci da sauransu. Haka bangaren karatun boko ma ba'a barsu a baya ba inda suke da masu Difloma, NCE, Digiri, Mastas, PhD har ma da Professor.

Lambar gidan waya na yankin ita ce 830.[1]

Karamar Hukumar Dandume ta jahar Katsina tana da Mazaɓu guda goma sha ɗaya (11) a karkashinta.

Ga jerin sunayen su kamar haka;[2]

  1. Dandume A
  2. Dandume B
  3. Dantankari
  4. Magaji wando A
  5. Magaji wando B
  6. Mahuta A
  7. Mahuta B
  8. Mahuta C
  9. Nasarawa
  10. Tumburkai A
  11. Tumburkai B


By Yusuf Sahabi Badole

Manazarta

gyara sashe
  1. "Post Offices- with map of LGA". NIPOST. Archived from the original on 2009-10-07. Retrieved 2009-10-20.
  2. https://nigeriadecide.org/polling_unit_category.php?state=Katsina&lga=Dandume