Dandume

Karamar hukuma kuma gari a jahar Katsina, Najeriya.

Dandume (ko Dan Dume ) karamar hukuma ce a cikin jihar Katsina, Najeriya. Hedikwatarta kuma tana cikin garin Dandume da ke yammacin yankin. a11°27′30″N 7°07′37″E / 11.45833°N 7.12694°E / 11.45833; 7.12694.

Dandume

Wuri
Map
 11°25′00″N 7°12′00″E / 11.4167°N 7.2°E / 11.4167; 7.2
Ƴantacciyar ƙasaNajeriya
JihaJihar Katsina
Labarin ƙasa
Yawan fili 422 km²
Bayanan Tuntuɓa
Kasancewa a yanki na lokaci

Tana da yanki na kimanin murabba'in km 422, da yawan jama'a 145,739 a ƙidayar shekara ta 2006. Sannan kuma mutanen karamar hukumar dandume suna gudanar da ayyukan noma Mutane ne masu al’adu iri ɗaya.

Lambar gidan waya na yankin ita ce 830.[1]

Karamar Hukumar Dandume ta jahar Katsina tana da Mazaɓu guda goma sha ɗaya (11) a karkashinta.

Ga jerin sunayen su kamar haka;[2]

  1. Dandume a
  2. Dandume b
  3. Dantankari
  4. Magaji wando a
  5. Magaji wando b
  6. Mahuta a
  7. Mahuta b
  8. Mahuta c
  9. Nasarawa
  10. Tumburkai a
  11. Tumburkai b

Manazarta gyara sashe

  1. "Post Offices- with map of LGA". NIPOST. Archived from the original on 2009-10-07. Retrieved 2009-10-20.
  2. https://nigeriadecide.org/polling_unit_category.php?state=Katsina&lga=Dandume