Bayajidda

Asalin mutumin da ya kafa masarautun Hausa

Bayajidda Wanda cikakken sunan shi shine(Abu Yazid ne) asalinsa ɗa ne ga sarkin Baghdad ne nasa cikin shi ana bayar da tarihin shi ne a matsayin wani jarumi wanda yazo daga Baghdad, ya zauna a cikin garin Daura inda a wancan lokacin anyi wata macijiya dake cikin garin take kuma takura ma mutanan dake cikin garin na daura inda macijiyar ke hana ibar ruwan rijiyar sai a rana guda daya ce ake ɗibar ruwa a rijiyar ta kusugu har yakai tana kashe mutanan da duk suke zuwa ibar ruwa a rijiyar ta kusugu in har ba ranar juma'a ba, a Wannan lokacin bayajidda ya kasan ce matafiyi ne tafiya ta kaishi cikin garin daura a inda ya sauka gidan wata tsohuwa me suna Ayyana dake cikin garin na daura a inda wata mace Ke sarautar garin na daura me suna Daurama, A Wannan lokacin Bayajidda ya isa garin a gajiye yunwa da kuma kishin ruwa na damun shi a inda tsohuwar daya sauka gidan ta, ta kawo masa abinci yaci ya Koshi ya nemi ta kawo masa ruwan sha ta nuna masa bata da ruwan da zata iya bashi yasha domin kowa dibar ruwan yake yana ajewa wanda har zai kaishi karshen satin dama kuma yazo ne cikin daren lahadi a inda tsohuwar Ke bashi labarin halin da garin yake baki daya wajen ruwan sha a inda ya nuna mata shifa zaije ya debo ruwan a cikin rijiyar nan wadda kowa Ke tsoro a duk fadin garin na daura jin hakan ya tayar ma tsohuwa da hankali sosai domin tasan in har yaje to ajalin sane yayi domin kuwa mutuwa zaiyi dole saboda haka tayi iya yinta wajen bashi haƙuri da kuma nuna mashi hatsarin da macijiyar take dashi amma ya kauda kai yaki ji,inda ya nemi tsohuwa ta bashi abun dibar ruwan ta yaje ya debo ruwa ba yadda ta iya tana kuka harda rike shi dan kada yaje amma sai da ya tafi a cikin daren wanda a Wannan lokacin kowa nata bacci harda munshari yaje bakin rijiyar ta kusugu ya jefa guga a cikin rijiya Sai yaji an rike yaja yaja yaji shiru yayi magana mutum ko aljani yaji shiru wanda hakan yasa ya jawo gugar shi da kyar da kyar har ya iso bakin rijiyar inda ya lura cewar macijiyar ce ta nan nade gugar wanda hakan yasa ya jawo ta macijiyar ta fasa kai wanda ke nuni da cewar zata cutar dashi inda yasa wukar shi mai kaifi ya sare mata kai ya raba kanta da kuma gangar jikin nata ya debi ruwan yasha kuma ya wanke jikin shi harma ya cika ma tsohuwar abun dibar ruwan ta ya kawo mata gida a wannan lokacin ne yabar waren takalmin sa guda daya a bakin rijiyar ta kusugu Wanda safiya nayi kowa ya fito dibar ruwa Sai ya koma gida a guje yaga abun mamaki macijiya a kwance wanda hakan yasa labari ya bade gari baki daya inda labari har ya kai fadar sarauniya Daurama wadda ke mulki a lokacin inda tazo da kanta ta gani abun yayi matukar yi mata dadi inda tasa a nemo mata wanda yayi wannan jarumtar domin ta biya shi tukwuici mai tsoka, a wannan lokacin ne gimbiya Daurama tasa kyauta mai tsoka inda akaita zuwa amma ba a samu, abun kamar da wasa har yakai fadar sarauniya Daurama inda tasa aka kawo warin kafar takalmin da bayajidda ya bari a bakin rijiyar ta kusugu kowa yazo yace nashi ne amma ina ba a samu ba wanda hakan yasa akayi shela duka Kauyukan dake karka shin ikonta da kowa yazo ya gwada takalmin nan da aka bari bakin rijiyar amma ba a samu wanda takalmin yayi ma daidai ba daga yayi kadan sai yayi yawa kowa yazo ba asamu wanda yayi ma daidai ba, daman kuma ya bar warin takalmin sane domin yasan dole a neme shi tsohuwa na ganin haka ta gane cewar toh ba kowa yayi aikin nan ba sai bakon ta daya sauka gidan ta na jiya da daddare ta tafi gida ta sanar dashi abun dake faruwa a gari wanda hakan yasa shima ya isa har cikin fadar sarauniya Daurama a inda shima yace shi ya kashe macijiya hakan yasa aka nemi shaida sai kuwa gashi ya fiddo kan maciya a jakar shi kuma ya gwada takalmin aka ga yayi mashi cif-cif da kafar sa ya fiddo dayen waren takalmin a cikin jakar shi yasa a nan ne fada ta cika da mamakin wannan bako gimbiya Daurama kuma ta cika alkawarin da tayi inda ta bashi kyautu ka masu yawa harma da rabin gari sarauniya Daurama ta bashi, karshe dai ya yanke shawarar zata aure shi bada dadewa ba abunka da daurin auren sarakai baifi sati biyu ba aka tara mutane aka daura aure aka sha bikin da ba a taba yin Irin saba a duk fadin daular ta Daura inda ya auri sarauniya Daurama.

Bayajidda
Rayuwa
Ƴan uwa
Abokiyar zama Daurama
Sana'a
Ƙofar shiga ta gidan Rumfa a shekara ta (2009) dake Kano, Najeriya.

Hakan yayi matukar burge mutanan dake ciki da Wajen masarautar ta Daura a inda suka zaman auren su har aka samu karuwa yaya da dama wanda ake kira da Hausa bakwai da kuma banza bakwai dake cikin fadin arewacin Nigeria.

Bibiyi Tarihin Zuwan Bayajidda da kafa masarautar daura ta sarauniya daurama.

Gabatarwa. Bayajidda ana bayar da tarihin shi a a matsayin wani jarumi wanda yazo daga Baghdad, ya zauna a cikin garin Daura inda ya kashe maciya, sannan kuma ya auri sarauniya Daurama

Tarihi gyara sashe

dafarko ya sauka a Borno a inda aka aurar masa da diyar Sarkin Daular Borno wato Mai,sai yaji raɗe-raɗin cewa sarkin zai kashe shi ya gaje sojojinsa. Sai matarsa ta ce su gudu, sai suka gudu cikin dare. sa'annan daga bisani yatafi zuwa kasar Hausa, Ance ya sauka a garin Daura cikin dare a gidan wata tsohuwa, inda kishirwa yakamashi, ya bukaci tasamo masa ruwa,a lokacin kuma bata da ruwa ruwan da take dashi ya kare sai ya tambaye ta, a ina ne akwai rijiya Sai ta gaya masa cewar akwai (wani katon maciji dake hana a dibu ruwa da daddare), amma Bayajidda bai tsorata ba, yaje rijiyar, Sarkin(Maciji) yafito ya nemi hana shi dibar ruwan, Bayajidda yayi fada dashi yasamu ya sare masa Kai a karshe dai ya kashe Sarki, kuma ya diba ruwarsa yakawo wa tsohuwa, ta cika da mamakin yadda yasamo mata ruwa acikin daren nan yakawo mata. Da gari yawaye, mutanen gari sunzo dibar ruwa, sai suka tarar da sarki a kwance, gashi ansare masa kai, al'umman gari suka fara murna da biki, cewar daga wannan lokaci babu abinda zai rika hanasu dibar ruwa, sai dai ba'asan wanda yayi wannan jaruntakar ba, har yasamu yakashe Sarkin, amma sai aka sama yamance da warin takalminsa kafa daya a gindin ko bakin rijiyar.

Mulki gyara sashe

Daga nan sai Sarauniyar Daura tayi alkawarin bayar da rabin gari ga duk wanda yayi wannan jarunta, kawai dayan sawun takalminsa Dan a tabbatar, sai tsohuwa tazo ta bayar da labarin abinda yafaru da daddare, aka kira Bayajidda Sarauniya ta aurar masa da kanta, Bayajidda daga bisani tanada yaro da akekira "Bawo" da "Biram" daga matarsa Sarauniyar Borno, da kuma wani yaron "karbogari" daga kuyangarsa Bagwariya.

Hausa bakwai da banza bakwai gyara sashe

Bawo ne yagaji mahaifinsa kuma yahaifa ya'ya shida(6), wadanda sune suka zama Sarakunan Daura, Katsina, Zazzau, Gobir, Kano da Rano. Wadannan, tareda Biram, wadda Shugaban ta shine dan Bayajidda daga wurin matarsa Sarauniyar Borno, sune suka Samar da "Hausa Bakwai" ko "Hausa 7". Dukda yake, dansa Karbogari wanda kuyangarsa BaGwariya ta Haifa masa, shima tanada ya Bakawai sune suka mulki Kebbi, Zamfara, Gwari, Jukun, Yoruba, Nupe da Yauri wadanda akekira da "Banza Bakwai" ko "Fake 7"[1][2]

Bibiliyo gyara sashe

  • Miles, William F. S. (1994). Hausaland divided : colonialism and independence in Nigeria and Niger. Ithaca: Cornell University Press. ISBN 978-0-8014-7010-3.

Manazarta gyara sashe

  1. Aigbokhai, S.O (1971). West African History for the Certificate Year. Great Brittain: George Allen & Unwin Ltd. p. 14. ISBN 0 04 966010 1.
  2. Miles, William F. S. (1994). Hausaland divided : colonialism and independence in Nigeria and Niger. p.45-46