Érico Roberto Mendes Alves Castro (an haife shi a ranar 22 ga watan Satumba 1992) ƙwararren ɗan ƙwallon ƙafa ne wanda ke taka leda a matsayin ɗan wasan tsakiya a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Petro Luanda. An haife shi a Portugal, yana wakiltar tawagar kasar Angola.

Érico Castro
Rayuwa
Haihuwa Oeiras (en) Fassara, 21 Satumba 1992 (31 shekaru)
ƙasa Portugal
Sana'a
Sana'a ɗan wasan ƙwallon ƙafa
Hanya
Ƙungiyoyi Shekaru Wasanni da ya/ta buga Ƙwallaye
 

Sana'a gyara sashe

Castro ya shafe yawancin aikinsa na buga wasa a Portugal a kungiyar kwallon kafa ta Campeonato de Portugal. Ya fara babban aikinsa da kulob ɗin Tires, kuma daga baya ya yi aiki tare da kungiyoyin Oeiras, Fátima, Aljustrelense, Real, Sintrense, Casa Pia, Felgueiras, da Louletano.[1] Ya koma Angola tare da Petro Luanda a ranar 23 ga watan Agusta 2021. [2]

Ayyukan kasa da kasa gyara sashe

An haife shi a Portugal, Castro dan asalin Angola ne. [3] Ya fara wasa da tawagar kasar Angola a wasan neman gurbin shiga gasar cin kofin duniya da ci 3–1 2022 a kan Gabon a ranar 8 ga watan Oktoba 2021.[4]

Hanyoyin haɗi na waje gyara sashe

  • Érico Castro at ForaDeJogo (archived)
  • Érico Castro at Soccerway

Manazarta gyara sashe

  1. Pereira, David (March 19, 2020). "O Blog do David: Érico Castro. Um tanque à solta no ataque do Louletano" .
  2. "Mercado: Avançado Érico Castro reforça o Petro de Luanda" . August 23, 2021.
  3. "World Cup 2022: Érico Castro called at the last minute to join the national team" . VerAngola .
  4. "FIFA" . FIFA . 2021-10-08. Retrieved 2021-10-18.