Monisade Afuye

Mataimakiyar Gwamnan jahar Ekiti

Monisade Christiana Afuye (an haife ta 28 ga watan Satumban 1958)[1] ƴar siyasar Najeriya ce wadda ta zama mataimakiyar gwamnan jihar Ekiti tun shekarar 2022.[2]

Monisade Afuye
Deputy Governor of Ekiti State (en) Fassara

16 Oktoba 2022 -
Bisi Egbeyemi (en) Fassara
Rayuwa
Haihuwa Ikere, 28 Satumba 1958 (65 shekaru)
ƙasa Najeriya
Harshen uwa Yarbanci
Karatu
Harsuna Turanci
Yarbanci
Pidgin na Najeriya
Sana'a
Sana'a ɗan siyasa da entrepreneur (en) Fassara
Imani
Addini Kiristanci
Jam'iyar siyasa All Progressives Congress

Tarihin Rayuwa

gyara sashe

An haifi Monisade Christiana Afuye a ranar 28 ga watan Satumban 1958 a Ikere-Ekiti, ƙaramar hukumar Ikere. Ta yi karatun firamare a Saint Joseph CAC Primary School Aramoko, Aramoko Ekiti, sannan ta yi karatun sakandare a makarantar Amoye Grammar School, Ikere-Ekiti. Ta samu difloma ta al'ada da babbar difloma a fannin harkokin gwamnati daga Crown Polytechnic, Ado Ekiti, jihar Ekiti.[1]

Manazarta

gyara sashe