Luizinho Luis
Luis Domingos Antonio Cazengue (an haife shi a ranar 11, ga watan Agusta 1969), ana yi masa lakabi da Luizinho, tsohon ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne na ƙasar Angola wanda ya fara aikinsa a Angola, kuma ya taka leda a Portugal.
Luizinho Luis | |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|---|
Rayuwa | |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Haihuwa | Portuguese Angola (en) , 11 ga Augusta, 1969 (54 shekaru) | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
ƙasa | Angola | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Karatu | |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Harsuna | Portuguese language | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Sana'a | |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Sana'a | ɗan wasan ƙwallon ƙafa | ||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
| |||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||||
Muƙami ko ƙwarewa | Ataka |
Sana'ar wasa gyara sashe
Cazengue ya fara aikinsa tare da Atlético Petróleos de Luanda a Girabola. A lokacin da yake aiki tare da kulob ɗin Luanda ya lashe gasar Girabola sau biyar daga shekarun 1986 zuwa 1990, kuma ya lashe Taça de Angola a shekarun 1987, da 1992. A cikin shekarar 1992, ya tafi ƙasashen waje zuwa Portugal don komawa kulob ɗin Lusitano GC na Segunda Liga. A cikin shekarar 1993, ya yi aiki tare da kulob ɗin CD Fatima.[1] A kakar wasa ta gaba, ya sanya hannu tare a kulob ɗin SC Braga na Primeira Liga, inda ya bayyana a wasanni 26 kuma ya zira kwallaye biyu.[2] Bayan zamansa a Primeira Liga ya shafe lokaci tare da kulob ɗin SC Lamego, Académico de Viseu FC, Clube Caçadores das Taipas, Lusitânia FC, da FC Oliveira do Hospital. A cikin shekarar 2002, an ba da shi rancensa ga kungiyar kwallon kafa ta Toronto Supra na Canadian Professional Soccer League. Ya buga wasansa na farko a ranar 29 ga watan Agusta, 2002 a wasan da suka yi da Durham Flames, kuma ya ci kwallo a ci 5-2.[3] Abin takaici a lokacin da yake aiki tare da Toronto kulob din ya kare a karshe a Eastern Conference, kuma ya kasa samun damar shiga bayan kakar wasa.
Ayyukan kasa da kasa gyara sashe
An zabi Cazengue a matsayin dan wasan kwallon kafa na kasar Angola na gasar cin kofin kasashen Afirka na shekarar 1996. Ya fito a gasar da Afrika ta Kudu, inda Angola ta sha kashi da ci 1-0 a wasan.[4][5]
Girmamawa gyara sashe
Kulob gyara sashe
- Petro Atlético
- Girabola: 1986, 1987, 1988, 1989, 1990
- Angola: 1987, 1992
Manazarta gyara sashe
- ↑ "Luisinho" . Futebol 365 . Retrieved 2015-12-26.
- ↑ "ForaDeJogo.net - Luisinho (Luís Domingos António Cazengue)" . ForaDeJogo. Retrieved 2015-12-26.
- ↑ Glover, Robin. "August 29, 2002 CPSL Toronto Supra vs Durham Flames" . www.rocketrobinsoccerintoronto.com . Retrieved 2015-12-26.
- ↑ "South Africa - International Matches 1996-2000" . RSSSF . Retrieved 2015-12-26.
- ↑ Strack-Zimmermann, Benjamin. "Luisinho" . www.national-football-teams.com . Retrieved 2019-03-27.